
Kimanin shugabannin ƙasashe 30 ne ake saran su gabatar da jawabinsu a wannan rana, duk da cewa da dama daga cikin shugabannin ƙasashe masu ƙarfin tattalin waɗanda kuma ke gurɓata muhalli basu halarci taron ba.
A jawabinsu, faraministan Girka Kyriakos Mitsotakis, ya ce ƙasashen Turai da sauran ƙasashe su samar da tsari na gaskiya ta yadda za a koma amfani da makamashi da baya gurɓata muhalli, duk da cewa hakan kuwa na buƙatar lokaci mai tsawo.
Shima da ya ke gabatar da nasa jawabin, faraministan Bahamas Philip Davis, ya ce tuni matsalar sauyin yanayi ta haifar da asarar rayuka da dukiya, amma har yanzu shugabanni sun gaza ɗaukar matakan da suka kamata wajen magance matsalar.
Ra’ayinsu yazo kusan dai-dai da takwaransa na Albania Edi Rama, wanda ke ganin rashin maida hankali daga ɓangaren hukumomi na maida hannu agogo baya, wajen tunkarar matsalar duk kuwa da illar da take da shi.
Iran kuwa ta bakin mataimakin shugaban ƙasar Shina Ansari, buƙatar ƙasashe ta yi da su kauda batun siyasa su mai da hankali wajen tattaunawar ilimi da musayar fasaha da kuma ɗage takunkuman da aka sanyawa wasu ƙasashe.
A nata bangaren, fadar Vatican da ta samu wakilcin babban sakatarenta, Cardinal Pietro Parolin, neman samar da tsarin tara kuɗaɗe da za a yi amfani da su don gina al’umma ta yi.
Dama dai tun a lokacin da Sakatare Janar na Majalisar Ɗinkin Duniya Antonio Guterres, ke gabatar da jawabinsa wajen buɗe taron, ya tunasar da shugabannin ƙasashen da ke halartar taron na COP29 cewa, lokaci yayi da za su bada gudunmuwarsu don kare afkuwar bala’o’in da sauyin yanayi ke haifarwa, domin a cewarsa lokaci na ƙure wa don takaita ƙaruwar yanayin zafi a duniya.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da muKu saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI