Nandi-Ndaitwah ta zama shugabar ƙasa mace ta farko a tarihin Namibia

Nandi-Ndaitwah ta zama shugabar ƙasa mace ta farko a tarihin Namibia

Nandi-Ndaitwah mai shekaru 72 wadda da ma ita ke riƙe da muƙamin mataimakiyar shugaban ƙasa, nasararta kai tsaye za ta sake tsawaita shekaru 34 na mulkin jam’iyyar ta SWAPO ne wadda ke jan ragamar ƙasar tun bayan samun ƴanci biya bayan nasarar kawo ƙarshen mulkin wariya na apartheid a shekarar 1990 ƙarƙashin jagorancin Afrika ta kudu.

Hukumar zaɓen Namibia ta ce Nandi-Ndaitwah ta samu kashi 57 ne yawan ƙuri’un da aka kaɗa a zaɓen na ƙarshen mako wanda dama ta na buƙatar aƙalla kashi 50 ne don samun nasara.

A jawabinta na farko bayan hukumar zaɓe ta bayyana ta a wadda ta yi nasara, Nandi-Ndaitwah ta ce al’ummar ƙasar sun zaɓi ɗorewar zaman lafiya da kwanciyar hankali baya ga tagomashin tattalin arziƙi fiye da komi.

Alƙaluman da hukumar zaɓen Namibia ta fitar sun nuna yadda ɗan takarar babbar jam’iyyar adawa ta IPC wato Panduleni Itula ya zo na biyu a zaɓen da jumullar kashi 26 na yawan ƙuri’un da aka kaɗa.

Netumbo Nandi-Ndaitwah na cikin ƴan gwagwarmayar da suka yi fafutukar samun ƴancin ƙasar a shekarun 1960.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Hulda da mu

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI


News Source:   RFI (rfi.fr)